BBC Hausa of Wednesday, 17 March 2021
Source: BBC
Ƴan Najeriya da dama sun yi ta bayyana albarkacin bakinsu a shafukan sada zumunta da muhawara kan rikicin da ya ɓarke tsakanin Musulmai da Kiristoci kan batun saka hijabi a wasu makarantun jihar Kwara.
A ranar Laraba ne fada ya ɓarke tsakanin Musulmai da Kiristoci a Makarantar Sakandare Baptist da ke birnin Ilori na jihar Kwara, a yankin tsakiyar Najeriya kan batun barin ƴan makarantar su sanya hijabi.
An ƙaddamar da maudu'i mai taken #Kwara da #Hijab a shafin sada zumunta na Twitter inda aka yi amfani da su fiye da sau sama da 12,000 da kuma sau sama da 6,000.
Me ake cewa a Tuwita?
Ra'ayoyi sun sha bamban a shafin Tuwita, yayin da wasu ke ganin laifin hukumomin makarantun, wasu kuwa laifin iyayen yaran suke gani.
Masu ganin laifin iyayen yaran na cewa idan har tsarin makarantun bai musu ba to kamata ya yi su cire su, musamman tun da sun san cewa makarantun na mabiya addinin kirista ne.
'As parents who want their children to wear hijab '
— Aisha Yesufu (@AishaYesufu) March 17, 2021
Religious combatants In Ilorin fighting for or against the Hijab should reserve their energy and protect their state from Bandits gradually moving in from Niger State.
— Senator Shehu Sani (@ShehuSani) March 17, 2021
I don't think Hijab should be a reason for a clash between Muslims and Christians in Kwara State, Muslim ladies should be allowed to wear Hijab to schools, provided the schools ain't owned by Christians, and Christian ladies shouldn't be forced to wear Hijab, it's very simple.
— F A A R E E S