BBC Hausa of Monday, 31 May 2021
Source: BBC
Mutanen Somaliland na fatan zaɓen ranar Litinin zai kasance mizanin samun karɓuwa ga ƙasashen duniya a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta kamar yadda mai sharhi game da yankin Mary Harper ta rubuta.
"Na matsu na kaɗa ƙuri'a ta," in ji ƴar shekara 15 Yasmin Abdi. "Ina jin kamar na girma na mallaki hankalina a yanzu, kusan kamar na mallaki wani ɓangare na ƙasata."
Cancantar yin zaɓe a cikin al'ummar da ake ɗaukar yara masu shekaru 15 da haihuwa a matsayin waɗanda suka mallaki hankalinsu, shekarun Ms Abdi daidai rabin shekarun Somaliland ne, wacce ta yi bikin cika shekara 30 a ranar 18 Mayu.
Tun ayyana ƴancin kai daga Somaliya, ba ta samu karɓuwa ba daga ƙasashen duniya amma tana ci gaba da tafiyar da harkokinta kamar ƙasa mai cin gashin kanta - tana da fasfo da kuɗinta da tuta da gwamnati da kuma sojoji.
"Somaliland na iya karewa a matsayin daya tilo a yankin gabashin Afirka da ke da kowane irin salon zaɓe na dimokaradiyya a wannan shekara," in ji Daraktan cibiyar Rift Valley, Mark Bradbury.
Mataimakin shugaban jam'iyya mai mulki Ahmed Dheere, shi ma ya goyi bayan kalaman Mr Bradbury. "Wannan zaɓe yana da muhimmancin sosai," cewarsa. "Za mu haskaka a yankin Afirka idan har muka yi nasarar yin zaɓe."
Somaliland na iya zama mafi mulkin dimokuraɗiyya fiye da wasu ƙasashe na yankin, amma tsarinta bai kammala cika ba.
Fiye da shekara 10 aka yi zaɓen ƴan majalisar. Ya kamata a gudanar da zaɓen kananan hukumomi, wanda za a gudanar a lokaci guda, shekaru hudu da suka gabata.
Babban jami'in jam'iyyar adawa ta Waddani, Hersi Ali Haji Hassan, ya ɗora laifin jinkirin kan ƴan majalisar dokoki.
"Yawancin ƴan majalisa suna da son kai da babakere. Sun yi maka ƙiba sosai a shekaru biyar a majalisa kuma ba su son sauka da kujerunsu. Kuma muna ɗora laifin ga gwamnati saboda ta cin ribar tsarin."
Kama ƴan jarida
Akwai wata matsalar kuma. A majalisar wakilan babu wani da ke wakiltar kaɓilu tsiraru, mace ɗaya ce kawai cikin ƴan majalisa 82, ko da yake wasu za su tsaya takara.
An kama ƴan adawa guda biyar dab da kaɗa ƙuri'a. Halayen gwamnati game da kafofin yada labarai suna da tauri, tare da musgunawa da kama ƴan jarida, sannan an rufe gidajen watsa labarai.
An yi ƙoƙari don hana jam'iyyun siyasa yin kusanci da kaɓilu tare da ba da shata cewa uku kawai za su iya shiga zaɓen majalisar dokoki.
Amma shugaban jam'iyyar da ke da'awar tabbatar da adalci da ci gaba (Justice and Development party), Faisal Warabe, ya yi gargaɗin cewa ƙabilanci na ci gaba da zama barazana.
"Tsarin ƙabilunmu bai dace da tsarin dimokuradiyya ba. dole mu wargaza shi. Idan ba haka ba Somaliland za ta koma kamar Yemen, inda ƙabilu za su yi hamayya da juna tare tarwatsa ƙasar," a cewarsa.
Mista Warabe yana son a rusa majalisar dattawa ta guurti, wacce ta ƙunshi da shugabannin manyan ƙabilun Somaliland.
"Mutanen da suke wurin tun 1993, kuma lokacin da wani dattijo ya mutu sai dansa ya maye gurbinsa. Wannan ba dimokiradiyya ba ne," in ji shi.
Mutanen da ke wurin su ne tun 1993, idan ɗaya daga cikinsu ya mutu ɗansa ke maye gurbinsa. Wannan ba dimokuraɗiyya ba ne," a cewarsa.
Yana da wahala a kwatanta abin da ke faruwa a Somaliland da Somaliya.
"Duk da shata iyaka, Somaliland (game da al'ummarta) tana da nisa da Somaliya, wadda ke ci gaba da nacewa kan cewa muna daga cikin yankinta amma har yanzu ba mu da ikon gudanar da zaɓe kai tsaye," in ji Abdi Ahmed wani ɗalibin jami'ar Hargeisa.