Vous-êtes ici: AccueilAfriqueBBC2021 05 14Article 450766

BBC Hausa of Friday, 14 May 2021

Source: BBC

Yadda aka biya kudin fansar fiye da $18m a Najeriya

Matsalar garkuwa da mutane dai ta zama ruwan dare a wasu sassan Najeriya Matsalar garkuwa da mutane dai ta zama ruwan dare a wasu sassan Najeriya

Wani kamfanin nazarin hadurra a Najeriya, ya yi kiyasi cewa an biya kudin da suka kai kimanin dala miliyan goma sha takwas, wato kwatankwacin fiye da naira biliyan bakwai, don karbar fansar mutanen da aka sace a kasar cikin shekaru goma da suka gabata.

Wasu dai na ganin adadin kudin na iya zarta haka, idan aka yi la'akari da yadda matsalar ke dada habaka da kuma yawan mutanen da akan sace ana neman a biya makudan kudin fansa kafin a sako su.

To, ko ya masana ke kallon wannan lamarin?

Na nemi jin ta bakin Farfesa Muhammad Kabir Isa malami a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria, kuma mai sharhi kan sha'anin tsaro: