Vous-êtes ici: AccueilOpinionsActualités2021 04 15Article 450231

BBC Hausa of Thursday, 15 April 2021

Source: BBC

Neymar zai ci gaba da taka leda a Paris St Germain

Dan kwallon Brazil, Neymar ya ce yanzu batun makomarsa a Paris St Germain kan tsawaita zamansa a Faransa ba wani babban lamari ba ne da ke jan hankali.

A shekarar 2017, Paris St Germain ta dauki Neymar daga Barcelona kan dalar Amurka miliyan 265.60 a matakin mafi tsada a fanni tamaula a duniya.

Dan kwallon tawagar Brazil ya ci Ligue 1 uku da French Cup biyu tun komawarsa Faransa da taka leda, kuma ya taka rawar gani da PSG ta kai wasan karshe a Champions League a bara.

Neymar wanda yarjejeniyarsa za ta kare a karshen Yunin badi, ya kira kungiyar ta Faransa da cewa ''gida ce a wuri na''.

Neymar ya ci wa PSG kwallo shida a gasar Zakarun Turai da ake buga wa, shi kuwa Kylian Mbappe ya zura takwas a raga a ba.

Ranar Talata PSG ta kai wasan daf da karshe a Champions League na bana, duk da doke ta 1-0 da Bayern Munich ta yi a Faransa.

Ranar Laraba kungiyar ta Faransa ta je ta ci Bayern Munich 3-2 a wasan zagayen farko a quarter final a Jamus.